in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yaba da yarjejeniyar da bangarorin Sudan ta kudu suka cimma
2018-07-27 09:41:35 cri
Mai magana da yawun babban sakataren MDD Stephane Dujarric ya ce, MDD ta yaba da yarjejeniyar da wasu bangarori na Sudan ta kudu suka cimma kan wasu batutuwa da suka shafi madufun iko. Ya ce wannan wani ci gaba ne a kokarin da ake na wanzar da zaman lafiya a kasar.

Koda yake Dujarric ya ce, duk da yarjejeniyar da wasu bangarorin na Sudan ta kudu suka cimma a birnin Khartomun na kasar Sudan, har yanzu ba a kai ga warware wasu batutuwa da bangarorin ke kadaddama kansu ba.

Kakakin na MDD ya ce, tawagar MDD dake Sudan ta kudu, za ta ci gaba da sanya-ido kan yadda ake wannan tattaunawa, yayin da a hannu guda kuma bangarorin da abin ya shafa ke kokarin ganin sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya mai dorewa. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China