in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kudu za ta binciki harin da aka kaddamar kan jami'an MDD
2018-07-26 09:39:59 cri
Gwamnatin Sudan ta kudu ta sanar da kafa wani kakkarfan kwamitin jami'an tsaro domin yin bincike game da hare-haren da aka kaddamar kwanan nan kan ma'aikatan bada agaji da kayayyakin MDD a yankin Upper Nile.

Michael Chiengjiek, ministan cikin gidan Sudan ta kudu, ya fadawa 'yan jaridu a Juba cewa, shugaban kasar Salva Kiir ya amince a kafa kwamitin domin binciko hare-haren da aka kaddamar ma'aikatan bada agajin.

Ministan ya ce taron da suka gudanar sun yi Allah wadai da kona helkwatar hukumar ta kasa da kasa dake Maban, a yankin Upper Nile.

A ranar Litinin ne, wasu matasan Maban suka afkawa ma'aikatan agaji da kayayyakin hukumar dake arewa maso yammacin kasar don nuna bacin ransu na rashin aikin yi a yankunan da suke, inda suka yi fito-na-fito da jami'an tsaro.

Hukumar kare hakkin bil adama ta MDD UNHCR da hukumar tallafawa 'yan gudun hijira ta MDDr a Sudan ta kudu sun yi Allah wadai da kaddamar da hare haren. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China