Jami'in watsa labarai na sojojin kasar Kanar Muhammad Dole ya bayyana cikin wata sanarwa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya samu kwafe cewa, sojojin sun yiwa 'yan bindigan kwanton bauna ne, inda suka yi nasarar kashe 20 daga cikinsu, wasu kuma suka arce da raunin harbin bindiga, baya da babura da dama da a kona. Kana sun kwace makamai da albarusai da babura, wayoyin salula da kuma shanu masu tarin yawa.
Ya kara da cewa, sojojin sun kuma yi nasarar kashe wasu jiga-jigan 'yan bindiga biyu Bello Danboko da Sani Maza a Yanwari kusa da mazabar Yankuzo da kauyen Mai Tukunya kusa da Dansadau dukkansu a jihar ta Zamfara.
A makon da ya gabata ne gwamnatin Najeriya ta tura jami'an tsaro dubu 1 da suka hada da sojojin sama da na kasa da 'yan sanda da masu tsaron fararen hula, da nufin kawo karshen hare-haren da 'yan bindigar ke kaiwa a kauyuka da garuruwa a jihar ta Zamfara. (Ibrahim Yaya)