in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Minister: Najeriya tana kokarin shawo kan matsalar tabarbarewa tsaro da ya addabi kasar
2018-08-03 09:49:07 cri
Ministan tsaron Najeriya Mansur Dan-Ali ya sanar da cewa, hukumomin tsaron kasar suna cigaba da yin iya bakin kokarinsu domin kawo karshen yanayin tabarbarewa tsaron da ake fama da shi a fadin kasar.

Dan Ali ya bayyana a Abuja babban birnin kasar cewa, an tanadi wata tawagar tsaro ta musamman mai taken "Operation SHARAN DAJI" inda aka tura ta zuwa yankunan dake makwabtaka da jahar Neja domin tabbatar da tsaro a dazukan jahohin arewa maso yammacin kasar da suka kunshin yankunan Zamfara, Sokoto da Birnin-Gwari.

Ya bayyana hakan ne bayan wata ganawar sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gudanar tare da manyan hafsoshin tsaron kasar, wanda ministan tsaron ya ce shi ne batu na baya bayan nan da taron majalisar kasar ya gudanar game da sha'anin tsaro a kasar.

A cewasa, an samar da karin dakarun tsaro na sojoji tare da tallafin jami'an tsaron tattara bayanan sirri, da nau'urorin tattara bayanan sirri karkashin rundunar tsaro ta 207 ta 'yan sandan kasar masu kai daukin gaggawa don wanzar da tsaro a kasar baki daya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China