in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Liu Zhenmin ya ja hankalin kasashen duniya game da illar daukar matakan sanyawa kasuwanni shinge
2018-07-20 10:35:09 cri
Mataimakin sakataren MDD mai lura da harkokin tattalin arziki da zamantakewar al'umma Liu Zhenmin, ya ja hankalin kasashen duniya game da illar dake tattare da daukar matakan sanyawa kasuwanni shinge, matakin da a cewar sa ka iya zama kalubale ga tsarin gudanar da kasuwanci tsakanin sassa daban daban.

Mr. Liu ya bayyana hakan ne, yayin wani zama na karawa juna sani game da yanayin tattalin arziki da cinikayyar kasa da kasa, da yadda hakan ke shafar ci gaban mai dorewa, wanda cibiyar raya tattalin arziki da zamantakewar al'umma ta MDD (ECOSOC) ta shirya.

Liu ya ce, ci gaban tattalin arziki kadai ba zai wadatar da bukatar al'ummun duniya ta cin gajiyar bai daya ba. Kuma duk da irin fadadar tattalin arziki da ake samu, a hannu guda duniya na fuskantar karin kalubale. Don haka ya dace kasashe daban daban su yi hadin gwiwa, wajen samar da ci gaba mai dorewa, da aiwatar da manufofin bai daya, karkashin dokoki da aka tsara masu cike da adalci, da daidaito, wadanda kuma za su baiwa kowa damar cin gajiyar kasuwanci tsakanin sassa daban daban.

An dai gudanar da zaman ne na manyan masana harkokin kasuwanci da cinikayya, a hedkwatar MDD dake birnin New York. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China