in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fitar da wani bangare na babban zaben kasar Zimbabwe
2018-08-01 11:39:38 cri
Hukumar zaben kasar Zimbabwe ZEC, ta bayyana sakamakon farko farko na babban zaben kasar da aka kada a jiya Talata, wanda ya nuna cewa jam'iyyar ZANU-PF mai mulki, na kan gaba da kujerun wakilci 6, yayin da jam'iyyar adawa ta MDC Alliance ke da guda daya.

Zimbabwen dai na da jimillar kujerun wakilci 210. Ana kuma sa ran kammala bayyana sakamakon zaben shugaban kasar da ya gabata nan da ranar Asabar 4 ga watan nan na Agusta.

Shugaban hukumar zaben kasar ta ZEC Priscilla Chigumba, ta ce hukumarta za ta ci gaba da bayyana sakamakon zaben da zarar sun tattara alkaluma. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China