in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tarayyar Afrika za ta sa ido sosai kan zabukan Zimbabwe
2018-07-11 11:16:40 cri
Tarayyar Afrika AU, ta ce za ta sa ido sosai kan zabukan shugaban kasa da na 'yan majalisu a Zimbabwe, wanda aka shirya yi a ranar 30 ga watan nan.

Wata sanarwar da tarayyar ta fitar jiya, ta ce bisa gayyatar gwamnati da hukumar zaben kasar, ta riga ta tura ayarin shirinta dake sa sanya ido kan harkokin zabe.

Sanarwar ta ce gudanar da sahihin zabe bisa tsarin demokradiyya da zaman lafiya a kasashe mambobinta abu ne mai muhimmanci wajen cimma manufofinta, da kuma daukacin burinta na tabbatar da samar da zaman lafiya da cigaba da dunkulewar nahiyar.

A watan da ya gabata ne AU ta tura jami'ai 5 masu zaman kansu, dake taimakawa wajen shirya zabe zuwa Zimbabwe, daga ranar 15 ga watan Yuni zuwa 8 ga watan nan domin bada taimako.

Haka zalika, ayarin shirinta dake sa ido kan zabuka mai mutane 14, da suka hada da manazarta 4 da masu sa ido kafin, yayin da kuma bayan zabe guda 10, sun isa Harare, babban birnin Zimbabwe a ranekun 3 da 5 ga watan nan da muke ciki. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China