in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Zimbabwe yana kiraye kirayen a zauna lafiya gabanin zaben kasar
2018-07-22 15:14:24 cri
Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa a jiya Asabar ya tunatar da magoya bayan jamiyyar ZANU-PF mai mulkin kasar dasu kauracewa duk wani nau'in bangar siyasa kasancewar jam'iyyar tana ta kokarin tsabtace harkokin siyasa da neman samun nasara ba tare da tashin hankali ba a zabukan kasar da za'a gudanar a ranar 30 ga watan Yuli.

Da yake jawabi ga dubban magoya bayan jam'iyyar a Marondera, dake gabashin lardin Mashonaland, Mnangagwa ya ce jam'iyyar ZANU-PF girmanta ya wuce ta dinga neman takalar rikici da kananan jam'iyyun kasar.

Mnangagwa ya fara jawabin nasa ne da bayyanawa taron gangamin irin shirye shiryen da jam'iyyar mai mulkin ke kokarin aiwatarwa nan da shekaru 5 masu zuwa har ma fiye. Ya ce daga cikin shirye shiryen akwai gagarumin aikin samar da lantarki da aikin hakar ma'adinai.

Yace gwamnati zata bada fifiko wajen zamanantar da aikin gona domin tabbatar da ganin manoman kasar sun samar da kyakkyawar yabanya.

Mnangagwa yayi alkawarin sake daga martabar kasar Zimbabwe a harkokin kasa da kasa bayan da kasar ta shafe shekaru masu yawa a matsayin saniyar ware. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China