in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala kada kuri'a lami lafiya a Zimbabwe
2018-07-31 10:21:14 cri
An kammala kada kuri'a jiya da daddare a Zimbabwe, inda hukumomin zabe suka bayyana cewa, masu kada kuri'a sun yi fitar dango a fadin kasar.

Kwamshinan hukumar zaben kasar Qubani Moyo, ya ce an kada kuri'a lami lafiya a fadin kasar, kuma matsalolin zabe kalilan aka samu, inda ya ce za a fara kidaya kuri'un bayan kammala zaben da misalin karfe 7 na dare a jiya.

Ya ce ana sa ran fara samun sakamakon zaben majalisar dokokin kasar da na hukumomin yankunan da safiyar yau Talata, yayin da na shugaban kasa zai kai zuwa ranar 4 ga watan Augusta mai kamawa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China