in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi maraba da kawo karshen cutar Ebola a DRC
2018-07-27 09:35:29 cri
Shugaban hukumar zartaswar kungiyar tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat, ya yi maraba da sanarwar da gwamnatin Jamhuriyar demokiradiyar Congo ta bayar a hukumance na kawo karshen barkewar annobar cutar Ebola a kasar.

Shugaban wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, ya ce a ranar 24 ga watan Yulin da muke ciki ne, ma'aikatar lafiyar Jamhuriyar demokiradiyar Congo ta ayyana kawo karshen yaduwar kwayar cutar Ebola a lardin Equatuer, bayan kwararan matakan da mahukunatn kasar suka dauka na dakile yaduwar cutar da ta bullo a yankunan kasar.

Idan ba a manta ba a ranar 8 ga watan Mayun wannan shekara ce, mahukuntan DRC suka sanar da sake bullo cutar a yankin Bikoro health, wanda shi ne na tara da cutar da sake bullo cikin shekaru 40 a kasar.

Sanarwar ta ce, tun kwanaki 42 da suka gabata rabon da a sake samun rahoton wanda ya kamu da kwayar cutar. Bisa dokokin hukumar lafiya ta duniya da ka'idojin lafiya na kasa da kasa, an kawo karshen cutar ke nan a kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China