in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yabawa tawagar wakilan Sin don babbar gudummawa da ta bayar ta fuskar zurfafa huldar dake tsakanin Sin da Afirka
2018-06-21 11:02:10 cri
Jiya Laraba, mataimakin shugaban kwamitin kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU Quartey Kwesi ya halarci bikin bankwana da shugaban tawagar wakilan kasar Sin dake kungiyar AU Kuang Weilin ya shirya, inda ya bayyana cewa, tawagar wakilan da kasar Sin ta turawa kungiyar AU ta zurfafa dangantakar zumuncin dake tsakanin Sin da Afirka, lamarin da zai bada gudummawa wajen habaka hadin gwiwa da mu'amalar dake tsakanin bangarorin biyu daga dukkan fannoni.

Haka kuma ya ce, tun lokacin da aka kafa tawagar wakilan kasar Sin dake kungiyar AU, ana ci gaba da karfafa hadin gwiwar a tsakanin Sin da Afirka, kuma tawagar wakilan Sin ta ba da babban taimako ga kungiyar AU wajen kafa yankin ciniki cikin 'yanci na nahiyar Afirka, da zirga zirgar mutane na mambobin kungiyar AU cikin 'yanci, da kuma kafuwar kasuwar sufurin jiragen sama ta Afrika da dai sauransu.

A nasa bangaren, jakada Kuang Weilin ya nuna cewa, cikin shekaru uku da suka gabata, an zurfafa huldar dake tsakanin kasar Sin da kungiyar AU, kuma hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin biyu ya sami babban ci gaba a fannonin ma'amalar dake tsakanin shugabanninsu, gina ababen more rayuwa, kiwon lafiya da kuma kiyaye zaman lafiya da dai sauransu.

An bude ofishin tawagar wakilan kasar Sin dake kungiyar AU ne a watan Mayun shekarar 2015, kuma jakada Kuang Weilin shi ne shugaba na farko na wannan tawaga. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China