in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta gargadi masu tsoma baki da su guji yin abubuwan da za su wargaza zaman lafiyar Somaliya
2018-05-28 09:47:19 cri
Shugaban gudanarwar kungiyar tarayyar Afrika (AU), Moussa Faki Mahamat, ya bayyana damuwa game da karuwar tsoma bakin wasu bangarorin duniya wadanda ba na Afrika ba, game da al'amurran da suka shafi harkokin cikin gidan kasar Somaliya.

Faki ya fada a lokacin tattaunawa da firaiministan Somaliya, Hassan Ali Khaire, a helkwatar kungiyar tarayyar Afrika dake Addis Ababa babban birnin kasar Habasha, ya ce tsoma bakin yana yin barazana ga zaman lafiyar da ake ginawa da kuma kokarin da ake yi a halin yanzu na tabbatar da zaman lafiya a Somaliya.

Ya ce tsoma bakin wata babbar barazana ce dake mayar da hannun agogo baya a kokarin da ake na hadin gwiwa tsakanin (AMISOM) da dakarun tsaron kasar Somaliya, inda ya bukaci dukkan masu shiga tsakani na kasashen waje da su guji yin dukkan abubuwan da za su wargaza shirin zaman lafiyar Somaliya.

Sanarwar ta ce, shugabannin biyu sun tattauna game da irin ci gaban da aka samu a halin yanzu bayan da gwamnatin Somaliya ta aiwatar da ajandar sauye sauye a harkokin siyasa, tattalin arziki da tsaron kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China