in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta taimakawa mambobin AU tunkarar wasu kalubalen muradun 2030
2018-07-17 11:02:15 cri
Wakilan kasashe mambobin tarayyar Afrika AU, sun bayyana wasu kalubale na musammam da kasashensu ke fuskanta wajen cimma muradun ci gaba masu dorewa na MDD da ake son cimmawa ya zuwa shekarar 2030 da kuma makamancinsu na AU da ake son cimmawa ya zuwa 2063, tare da duba yuwuwar samun mafita game da damuwarsu.

Wakilan sun hadu ne a ofishin AU na MDD, domin sauraron bayanai daga mambobin majalisar ta yadda za su samu darasin da za su koya.

AU ce ta bukaci a gudanar da taron a gafen taron manyan jami'ai kan nazarin aiwatar da muradun ci gaba masu dorewa na MDD a duniya, wanda ke gudana daga ranar 16 zuwa 18 ga watanan da muke ciki a hedkwatar MDD.

Taron na da nufin ba kasashe damar samun darasi daga bayanan da aka samu kamar na nazarin da kasashen mambobin AU suka yi. An bukaci kasashen sun bayyana darussan da suka samu da kuma kyawawan ayyuka da suka yi wadanda suka hada da na kirkire-kirkire da ayyukan masu ruwa da tsaki da na hadin gwiwar da kuma na tabbatar da yadda muradun za su dace da kasashensu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China