in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu rajin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta kudu sun yi kira da a kyautata dabarun kawo karshen tashin hankali
2018-07-20 11:10:12 cri
Masu rajin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta kudu, sun yi kira da a kyautata dabarun kawo karshen tashe tashen hankula a kasar, matakin da a cewar su shi ne kan gaba, wajen ganin bayan dumbin asarar rayuka da kasar ke fama da shi.

Da yake tsokaci game da wannan batu, mataimakin shugaban cibiyar sanya ido game da al'amuran da suka jibanci wanzar da zaman lafiya ko JMEC a takaice Augostino Njoroge, ya ce ya kamata kasashen dake shiga tsakani wato Sudan da Uganda, su kara azama wajen kawo karshen batutuwa da ake da sabani a kan su.

Mr. Njoroge ya ce wanzar da zaman lafiya na bukatar manufofi masu dorewa. Don haka ya wajaba a dauki matakan shawo kan kashe kashen rayukan jama'a.

An dai gudanar da zaman na karawa juna sani ne na yini hudu, a birnin Juba, fadar mulkin Sudan ta kudu. Taken taron shi ne "Gaggauta wanzar da zaman lafiya ta hanyar fadakar da matasa game da yanayin da ake ciki a Sudan ta kudu". Ya kuma samu halartar dalibai 200, karkashin lemar shirin wanzar da zaman lafiya da ci gaba na WPDI. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China