in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta kudu ta shirya tsaf don karbar bakuncin taron BRICS
2018-07-24 20:58:52 cri
Minista mai lura da al'amuran da suka shafi hadin gwiwar kasa da kasa a Afirka ta kudu Lindiwe Sisulu, ya ce kasar sa ta shirya tsaf, don karbar bakuncin taron kasashen kungiyar BRICS karo na 10 da zai gudana tsakanin ranekun 25 zuwa 27 ga watan nan na Yuli.

Da yake bayyana hakan ga manema labarai a jiya Litinin, Mr. Sisulu ya jaddada muhimmancin aiwatar da manufofin tattalin arziki a bude, tare da baiwa dukkanin kasashe damar shiga a dama da su, a harkokin da suka jibanci dunkulewar duniya, kamar yadda hakan ke kunshe cikin sanarwar da zaman ministocin wajen kasashe masu samun bunkasar tattalin arziki na watan Yuni ya ayyana.

Taron BRICS dake tafe zai samu halartar shugabanni kasashe mambobin kungiyar da suka hada da Brazil, da Rasha, da India, da China da Afirka ta kudu, wadanda ake sa ran za su tattauna game da matakan tunkarar kalubalen da ke fuskantar duniya baki daya. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China