in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za'a kaddamar da tauraron dan adam ta cube mafi girma a Afrika
2018-04-18 11:11:36 cri
Hukumomin sun tabbatar da cewa an kammala shirye shiryen kaddamar da tauraron dan adam mafi girma na cube a Afrika.

Ministan kimiyya da fasaha na kasar Afrika ta kudu Mmamoloko Kubayi-Ngubane, shi ne ya sanar da hakan, wanda kuma ya halarci bikin a jami'ar fasaha ta Cape Peninsula University of Technology (CPUT) dake birnin Cape Town, inda za'a aika da tauraron dan adam din zuwa Indiya, inda daga can ne kuma za'a harba tauraron a watan Yuli.

Tauraron dan adam din mai nauyi kilogram 4, wanda aka fi sani da ZACUBE-2, jami'ar ta CPUT ne ta kera shi tare da hadin gwiwar cibiyar nazarin fasaha ta French South African Institute of Technology.

Za'a yi amfani da tauraron dan adam din wajen bincike a tekun Afrika ta kudu da kuma gano wutar daji ta hanyar na'urar daukar hoto wanda cibiyar nazari da binciken kimiyya ta (CSIR) ta kera. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China