in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya aika da wasikar taya murnar bude taron dandalin tattaunawa tsakanin jama'ar Sin da Afirka
2018-07-23 14:02:25 cri

Yau ne aka kaddamar da taro karo na biyar na dandalin tattaunawa a tsakanin jama'ar Sin da Afirka a birnin Chengdu na kasar Sin, inda Shugaban kasar Xi Jinping ya aika da sakon taya murnar kaddamar da taron

A cikin wasikar, Shugaba Xi ya nuna cewa, dandalin tattaunawa a tsakanin al'ummar Sin da Afirka wata muhimmiyar gada ce a tsakanin jama'ar bangarorin biyu. Tun bayan da aka kafa dandalin a watan Agusta na shekarar 2011, dandalin ya samu babban ci gaba bisa ka'idoji uku wadanda suka hada da "kara dankon zumunci a tsakanin jama'a, da inganta hadin gwiwa, da kokarin tabbatar da zaman lafiya a duniya". Dandalin ya kuma taka muhimmiyar rawa ga cudanya da hadin kai a tsakanin jama'ar Sin da Afirka.

Bugu da kari Xi ya jaddada cewa, ana daukar batun "tattara karfin jama'a don kara azama ga aminci da fahimta a tsakanin Sin da Afirka" a matsayin babban taken taron na bana, wanda zai inganta mu'amala da hadin kai a tsakanin jama'ar bangarorin biyu sosai.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China