in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shirya bikin nune-nunen littattafan kasar Sin a Senegal
2018-07-21 14:47:28 cri
A ran 19 ga wata, agogon wurin, aka kaddamar da "bikin sanin kasar Sin na shekarar 2018, nune-nunen littattafan kasar Sin" a dakin adanar kayayyakin tarihi na nune-nunen al'adun bakaken fata na Senegal a Dakar, babban birnin kasar Senegal.

A yayin bikin, an yi nune-nunen littattafai 1589 da aka fassara su daga Sinanci zuwa harshen Faransanci. Abubuwan dake kunshe cikin wadannan littattafai sun shafi harkokin siyasa, tattalin arziki, al'adu da dai sauransu na kasar Sin. Sannan an kuma kafa wani dandali na musamman, inda aka yi nune-nunen littattafai game da shugaba Xi Jinping na kasar Sin, kamar littafi na farko da na biyu game da batun mulkin kasa da tafiyar da harkokin siyasa, da irin jawaban da shugaba Xi Jinping ya gabatar a yayin wasu muhimman bukukuwan kasa da kasa. Bugu da kari, an kuma yi nune-nunen wasu littattafai game da babban burin da kasar Sin take kokarin cimmawa, da hanyoyin neman ci gaba da kasar Sin take bi, da ilimomin jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da shawarar "ziri daya da hanya daya", ta yadda al'ummomin kasar Senegal za su iya kara sani da kuma fahimtar kasar Sin ta yanzu yadda ya kamata. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China