in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta tura jami'an sa ido kan harkokin zabe zuwa Senegal
2017-07-22 12:05:30 cri
Tarayyar Afrika ta tura jami'anta dake sa ido kan harkokin zabe zuwa Senegal, domin sanya ido kan zabukan 'yan majalisar dokokin kasar da aka shirya yi a ranar 30 ga watan Yuli.

Wata sanarwa da Tarayyar ta fitar jiya Juma'a, ta ce shugaban hukumar kula da ayyukanta Moussa Faki Mahamat, ya tura jami'an ne biyo bayan gayyatar da gwamnatin kasar dake yammacin Afrika ta mika Tarayyar, kuma jami'an za su kasance a kasar daga ranar 22 ga watan Yuli zuwa 4 ga watan Augusta.

An zabo jami'an ne daga cikin mambobin kwamitin wakilai na dindin-din na AU da majalisar dokokin tarayyar da hukumomin kula da zabe da kungiyoyin al'umma dake aiki kan harkokin da suka shafi demokuradiyya da shugabanci da zabuka a Afrika da masana da kuma masana harkokin zabe masu zaman kansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China