in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ta kai ziyara kasar Ghana
2018-07-21 14:14:22 cri
Bisa gayyatar da jam'iyyar New Patriotic ta kasar Ghana ta yi mata, a tsakanin ranaikun 19 da 21 ga watan, mataimakiyar shugaban hukumar kula da harkokin cudanya tsakanin jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da jam'iyyun siyasa na kasashen ketare madam Xu Lvping, ta shugabanci wata tawagar wakilan JKS zuwa ziyara a kasar Ghana.

A lokacin da tawagar ke ziyara a kasar Ghana, mataimakin jagoran jam'iyyar New Patriotic ta Ghana, kuma mataimakin shugaban kasar Mahamudu Bawumia, da shugaban kwamitin jam'iyyar na kasar Ghana Mr. Freddie Blay da kuma John Boadu, babban sakataren jam'iyyar sun gana da madam Xu Lvping, da sauran mambobin tawagar JKS.

Sannan tawagar JKS ta shirya wani taro, inda aka fadakar da Tunanin Xi Jinping, game da tsarin mulkin na gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin a sabon zamani da ake ciki. A waje daya kuma, bangaren Ghana ya taya murnar cin nasarar shirya wani taron kara wa juna sani, tsakanin manyan jagororin jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da na jam'iyyun siyasa na kasa da kasa. Ya kuma bayyana fatansa na karfafa yin musayar ra'ayoyi da fasahohin mulkin kasa, da tafiyar da harkokin siyasa tsakanin jam'iyyun biyu, ta yadda za a iya daga huldar dake tsakanin jam'iyyun siyasar biyu zuwa wani sabon mataki. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China