in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta maido ministan da aka sallama bisa zargin magudin visa kan mukaminsa
2018-07-10 10:09:59 cri
A jiya Litinin shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo ya mayar da mataimakin ministan matasa da wasanni na kasar Pius Enam Hadzide, kan mukaminsa wanda aka sallama bisa zargin aikata magudi game da takardun izinin shiga kasar Australia.

Fadar shugaban kasar ta bada sanarwar cewa ta dauki wannan mataki ne bayan kammala bincike game da zargin wanda sashen binciken laifuka na hukumar 'yan sandan kasar Ghanan ya gudanar.

Haka zalika an maido shugaban hukumar wasannin kasar Kwadwo Baah-Agyemang wanda aka kora daga mukaminsa, bayan kammala wani bincike wanda yayi sanadiyyar damke wasu 'yan kasar Ghanan kimaini 60, bayan an zargesu da yunkurin shiga kasar Australia da takardun izini na bogi a lokacin gasar wasannin Commonwealth ta bana.

Sakamakon rahoton binciken, wanda aka mikawa shugaban kasar a Juma'ar data gabata wato 6 ga watan Yulin shekarar 2018, ya nuna cewa, ba'a samu wadanda ake zargin da aikata laifin da ake tuhumarsu dashi ba, kamar yadda sanarwar da Eugene Arhin babban daraktan yada labarai na ofishin shugaban kasar ya sanyawa hannu. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China