Rahotanni na cewa, tun a ranar 18 ga wata aka fara ruwan sama a Ghana, abun da ya haddasa ambaliyar ruwa a wurare daban-daban. Daga cikinsu, ambaliyar ta fi yawa a birnin Accra, inda gine-gine da dama suka lalace, al'amarin da ya tilastawa mazauna da dama kaura.
Kwararru a kasar sun bayyana cewa, yanayin shimfidar kasa a Accra ya yi kasa sosai, sannan rashin kyan tsarin magudanan, baya ga wasu gine-gine da aka yi ba bisa ka'ida ba, da bola da suka toshe magudanan ruwa, sun kara tsananta halin da ake ciki.
Jami'in ya ce hukumar ta bukaci gwamnati da gyara magudanan ruwan tare da rushe wadancan gine-gine don tinkarar iftila'in. (Amina Xu)