Rundunar 'yan sandan jihar ta tabbatar da aukuwar wannan lamari a ranar Talata. Da yake karin haske game da hakan, kakakin rundunar David Misal, ya ce mahukuntan jihar sun ba da umarnin rufe kasuwar ta Iware. Kuma tuni aka fara gudanar da bincike domin gano musabbanin aukuwar lamarin.
Kawo yanzu dai ba a kama kowa ba, sai dai 'yan sanda na ci gaba da nazari tare da tattara bayanai. (Saminu Hassan)