in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 44 sun mutu yayin da wasu 20 suka bata sanadiyyar ambaliyar ruwan da ta auku a jihar Katsinan Nijeriya
2018-07-17 09:15:11 cri
Ambaliyar ruwa da mamakon ruwan sama ya haifar a karshen makon da ya gabata, ta yi sanadin mutuwar mutane 44 tare da batan wasu 20 a jihar Katsina dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Gwamnan jihar Aminu Belllo Masari, ya shaidawa manema labarai jiya cewa, sama da gidaje 500 ne suka lalace a yankin karamar hukumar Jibiya dake jihar.

Aminu Masari, ya ce gwamnati ta tsugunar da wadanda iftila'in ya shafa a wata makarantar firamare dake yankin.

A cewarsa, ya sanar da gwamnatin tarayyar kasar game da iftila'in, ya na mai jadadda cewa tuni hukumar bada agajin gaggawa ta kai manyan motoci 13 shake da kayakin jin kai da za a raba ga mutanen.

A nasa bangaren, shugaban kasar Muhammadu Buhari, ya bayyana damuwa da bakin ciki game da aukuwar iftila'in da ba a taba gani ba a jihar Katsina da ma wasu sassan kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China