in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Nijeriya ta musanta batan wasu dakarunta sanadiyyar kwantar baunan da mayakan Boko Haram suka yi musu
2018-07-17 09:09:42 cri
Rundunar sojin Nijeriya, ta musanta wani rahoto da ke cewa, wasu dakarunta sun bata biyo bayan kwantar baunan da mayakan Boko Haram su ka yi musu a karshen makon da ya gabata.

Kakakin rundunar Texas Chukwu, ya musanta rahoton da cewa ba gaskiya ba ne, inda ya ce babu wani soja da ya bata yayin kwanatar baunan da ta auku a yankunan Kwakwa da Chingori na karamar hukumar Baman jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Kakakin ya ce suna zargin mayakan Boko Haram da yunkurin kai wa sojoji hari a wadancan yankunan sanadiyyar kafewar da motocinsu suka yi saboda yanayin hanya.

Ya kara da cewa, 'yan ta'addan sun kuma yi yunkurin tafiya da motocin nasu, amma kuma sojojin tare da taimakon takwarorinsu na sama, sun yi nasarar fatattakar mayakan. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China