in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban Najeriya ya kaddamar da kamfanin simintin da Sin ta gina
2018-07-18 09:42:07 cri
Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya kaddamar da kamfanin simintin wanda kamfanin kasar Sin ya gina mallakar rukunin kamfanonin BUA.

Aikin gina kamfanin wanda ya lashe dala miliyan 350, dake yankin Kalambaina a jihar Sokoto a arewa maso yammacin kasar, ya kasance wata babbar cibiyar fitar da siminti zuwa kasashen ketare a shiyyar, wanda kamfanin Sinoma na kasar Sin ya gina.

Kamfanin zai iya samar da adadin siminti metric ton miliyan 1.5 a duk shekara, kana zai samar da ayyukan yi na kai tsaye kimanin 2,000 da kuma wasu ayyukan na wucin gadi kimanin 10,000 a fadin kasar.

Mataimakin shugaban kasar ya bukaci rukunin kamfanonin na BUA da su hada kai da sauran kamfanonin siminti don rage farashin simintin a kasar.

Kaddamar da kamfanin simintin ba wai nasara ce ga rukumin kamfanonin BUA kadai ba, har ma ga kamfanin simintin da tattalin arzikin Najeriya, in ji Osinbajo.

Ya ce nan da wasu 'yan shekaru masu zuwa kasar za ta samu gagarumin cigaba ta fuskar bunkasuwar kayayyakin more rayuwa. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China