Da yake tabbatar da hakan, shugaban hukumar ba da agajin gaggawa na jihar ta Katsina Aminu Waziri, ya ce an samo gawawwakin mutane 52 daga kauyuka 5, kana ana ci gaba da neman wasu mutanen 20. Jami'in ya ce an zakulo wasu gawawwakin ne daga karkashin gine gine da suka fadi sakamakon mamakon ruwa da ya haddasa rushewar gidaje masu yawa. Yayin da kuma aka samo gawawwakin wasu su 24 a wasu kauyuka 2 dake jamhuriyar Nijar mai makwaftaka da yankin, bayan da ruwa ya yi awon gaba da su.
Sama da gidaje 500 ne suka lalace, kana mutane kusan 5,000 suka rasa matsugunnansu, sakamakon wannan ibtila'i da ya auku. (Saminu Hassan)