Abubuwan da ake fatan tattaunawa a taron da zai gudana daga goben 18- 19 ga watan Yuli, sun hada da rawar da kafofin watsa labarai ke takawa wajen karfafa kawancen kungiyar, da karfafa sabon hadin gwiwar kafofin watsa labarai a kasashen na BRICS da ma hadin gwiwar kafofin watsa labarai tsakanin BRICS da Afirka.
Dandalin wani bangare ne na taron kolin kasashen BRICS karo na 10 da za a gudanar daga ranar 25-27 ga watan Yuli a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu, inda za a canja shugabancin kungiyar a shekarar 2018. (Ibrahim)