in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kenya za ta nemi kasashen Afirka da su karfafa matakan kare giwaye
2018-07-15 15:34:52 cri
Babbar sakatariya a ma'aikatar yawon shakatawa da kare dabbobin dawa ta kasar Kenya, Margaret Mwakima ta bayyana cewa, mahukuntan kasar na shirin tattaunawa da sauran kasashen Afirka don ganin sun karfafa matakan da suke dauka na kare giwayensu dake daf da karewa a ban kasa.

Jami'ar wadda ta shaidawa 'yan jaridu hakan a birnin Nairobin kasar Kenya, ta ce yanzu haka kasar dake kudancin Afirka ba ta haramta cinikin hauren giwa a cikin gida ba, kuma hakan na iya kassara kokarin da ake na kare giwayen dake nahiyar ta Afirka. Mwakima ta ce, ya zuwa yanzu, sama da kasashen Afirka 30 da Allah ya hore musu albarkatun giwaye dake tsakiya da yammacin Afirka na goyon bayan matakan da Kenya ke dauka na kare rayukan giwayen.

Bayanai na nuna cewa, an sanya adadin giwayen da kasashen Botswana da Namibia da Afirka ta kudu suke da su a cikin muhimmiyar takarda ta biyu na taron cinikayyar kasa da kasa game da dabbobin dake daf da karewa a muhallin halittu (CITES), wannan na nufin cewa, an ba su damar yin cinikin hauren giwa, a dai-dai gabar da aka sanya giwayen dake ragowar kasashen Afirka cikin muhimmiyar takarda ta farko wadda ta haramta cinikin hauren giwa.

Jami'ar ta kuma bayyana cewa, galibin kasashen Afirka, sun amince a sanya dukkan giwayen cikin muhimmiyar takarda ta farko a yayin taron CITES da zai gudana a watan Mayun shekarar 2019 a Sri Lanka. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China