in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dandalin cinikayya ta intanet na kasar Kenya na duba yiwuwar shiga kasuwannin nahiyar Afrika
2018-07-10 09:45:10 cri
Dandalin cinikayya ta intanet na kasar Kenya wato Kilimali, ya ce ya na shirin fadada zuwa sauran sassan nahiyar Afrika ya zuwa 2022.

Shugban dandalin Yang Tao, ya ce kamfanin da aka kafa a shekarar 2014, ya fara aiki a kasashen Uganda da Nijeriya a bara.

Yang Tao ya shaidawa wani ayarin Sinawa masu zuba jari dake neman damarmaki a bangaren cinikayya ta intanet na kasar Kenya cewa, suna shirin shiga dukkan kasashen Afrika ya zuwa karshen 2022, domin biyan bukatar cinikayya ta intanet da ke karuwa.

Ya kara da cewa, an fara kafa dandalin ne a Kenya la'akari da yadda kasar ta fi kowacce kyan yanayin kasuwanci a nahiyar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China