in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kenya na kokarin jan hankalin kasar Sin ta zuba jari a bangaren masana'antu
2018-06-13 10:43:33 cri
Gwamnatin kasar Kenya ta sanar da shirinta na jan hankalin jarin kasar Sin a bangaren masana'antun kasar dake gabashin Afrika.

Sakataren ma'aikatar masana'antu ta kasar Adan Mohamed, ya shaidawa wani taro kan cinikayya jiya a Nairobi cewa, kasar ta shirya abubuwan da za su ja hankalin masu zuba jari da suka hada da matakan haraji da raya ababen more rayuwa, don zamar da kasar wuri mafi arhar sarrafa kayayyaki.

Ya ce suna son masu masana'antu na kasar Sin, su taimkawa Kenya cimma burinta na zama jagora a fannin fitar da kayayyaki zuwa sauran sassan duniya.

Adan Mohamed, ya ce masu masana'antun na kasar Sin za su iya cin gajiyar arhar kudin kwadago domin samar da kayayyaki a cikin kasar da ma kasuwannin kasashen waje.

Ya ce kasar ta riga ta kaddamar da yankin raya tattalin arzikin na farko, wanda ya samar wa masu zuba jari ababen more rayuwa masu inganci irin na sauran kasashen duniya, domin su samar da hajojin da za su yi takara a kasuwanni duniya.

Har ila yau, ya ce an yarjewa masu zuba jari fitar da ribarsu zuwa kasashensu ba tare da wani tarnaki ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China