in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Eritrea ya ziyarci rukunin masana'antun Hawassa da Sin ta gina a Habasha
2018-07-15 15:03:55 cri
Jiya Asabar ne shugaba Isaias Afwerki na kasar Eritrea ya ziyarci rukunin masana'antun saka tufafi na Hawassa dake kudancin Habasha da kamfabin kasar Sin na CCECC ya gina.

Shugaba Afwerki ya ziyarci rukunin masana'antun ne bayan halartar wata gagarumar liyafar maraba da firaminista Abiy Ahmed da shugaban kasar Habashan Mulatu Teshome suka shirya masa a fadar shugaban kasar.

A cewar shugaban ma'aikata a ofishin firaministan Habasha Fitsum Arega, firaminista Ahmed ya bayyana rukunin masana'antu na Hawassa a matsayin wata alama ta ci gaban masana'antun kasar, kuma ya kasance abin koyi ga ragowar rukunonin masana'antun dake sassan kasar, duba da irin nasaraorin da ya cimma tun lokacin da aka kaddamar da shi a watan Yulin shekarar 2016, ta hanyar janyo hankulan manyan kamfanonin saka tufafi na duniya cikin kasar.

A baya gwamnatin kasar Habasha ta bayyana cewa, da zarar ya fara aiki rukunin masana'antun zai samar da kudaden shigar da suka tassama dala biliyan 1 a duk shekara.

Rahotanni na nuna cewa, a duk lokacin da shugabannin Afirka suka ziyarci kasar Habasha, su kan je rukunin masana'antun, shugaba na baya-bayan da ya ziyarci rukunin masana'antun na Hawassa, shi ne shugaba Paul Kagame na Rwanda,wanda ya kai ziyara a watan Mayun wannan shekara. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China