in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: yawan mutanen dake zama a manyan garuruwa da birane ya karu a 'yan shekarun nan
2018-07-12 13:37:40 cri
Wani rahoto da shirin kula da muhalli na MDD ya fitar ya nuna cewa, yawan mutanen dake zama a manyan garuruwa da birane ya karu a 'yan shekarun nan, har ma ana tunanin cewa, nan da shekarar 2030 adadin zai kai kaso 60 cikin 100 na daukin al'ummar duniya, kana nan da shekarar 2050 adadin zai kai kaso 66 cikin 100.

Rahoton daya ne daga cikin abubuwan da aka bayyana a dandalin shugabannin siyasa game da shirin ci gaba mai dorewa da ke gudana a halin yanzu, wanda ke bitar ajandar da MDD ke fatan cimmawa nan da shekarar 2030, game da manufofin ci gaba mai dorewa guda 17.

A cewar rahoton, an yi kiyasin cewa daga shekarar 2010 zuwa 2050, za a samu karuwar al'umma biliyan 2.5 zuwa 3 kan yawan al'ummar dake zaune a birane a fadin duniya.

Rahoton ya kuma yi hasashe game da samun bunkasuwa a yankuna marasa ci gaba, kamar yankunan gabashi da kudancin Asiya da kasashen Afirka dake kudu da hamadar sahara. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China