in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An hallaka kusan mutane 80 a arewacin Najeriya a wannan mako
2018-07-12 09:38:20 cri
Kimanin mutane 80 ne aka tabbatar da mutuwarsu a wasu hare-haren da aka kaddamar a arewacin Najeriya a wannan mako, kamar yadda kididdigar da jami'an kasar suka sanar a jiya Laraba.

Hare-haren wadanda aka kaddamar a ranakun Litinin da Talata a shiyyoyin arewa maso gabashi da arewa maso yammacin kasar, galibin an kaddamar da hare-haren ne a wasu kauyuka dake makwabtaka da juna.

Sama da mutane 50 ne aka hallaka a hare-haren da masu dauke da makamai suka kaddamar a wasu yankunan dake kan iyakokin jahohin Adamawa da Taraba, 'yar majalisar jihar Adamawa Sodomti Tayedi, ta tabbatar da hakan ga manema labarai.

Ta ce sakamakon wasu hare-hare a yankunan karamar hukumar Numan, yankin da take wakilta a majalisar dokokin jihar, mazauna yankunan wadanda galibinsu manoma ne sun tsere daga yankunan, sun bar gonakinsu.

A wani labarin makamancin wannan, hukumar bada agajin gaggawa ta kasa ta ce a kalla an samu gawarwakin mutane 26 sakamakon wasu hare-hare da aka kaddamar a cikin kwanaki biyu wadanda ake zargin barayin shanu ne suka kaddamar a jihar Sokoto dake arewa maso yammacin kasar.

Mazauna yankin sun tabbatar da cewa an yi awon gaba da shanu masu yawa kana an kona gidaje a lokacin da maharan suka afkawa kauyen Gandi a yankin Rabah da yammacin ranar Litinin. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China