in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 21sun bata sanadiyyar hatsarin kwale-kwale a Nijeriya
2018-07-10 09:33:35 cri
Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Sokoto dake arewa maso yammacin Nijeriya, ta ce masu linkaya sun gano gawar mutum guda, yayin da mutane 21 suka bata, biyo bayan hatsarin kwale-kwale da ya auku a jihar.

Shugaban hukumar Ibrahim Dingyadi, ya ce an ceto mutane 8 a hatsarin da ya auku sanadiyyar kifewar kwale-kwale a ranar Asabar da ta gabata.

Ibrahim Dingyadi, ya shaidawa manema labarai cewa, al'amarin ya auku ne a lokacin da kwale-kwalen mai fasinjoji 30 ya kife a kan hanyarsa ta zuwa kogin Bafarawa na jihar.

Ya kara da cewa an umurci masu linkayar da su nemo ragowar mutanen 21.

Yanzu haka dai, kogin Bafarawa, inda hatsarin ya auku, na matsayin koli saboda yanayin damina da ake cikin a Nijeriya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China