in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan wasan guje guje da tsalle tsalle na Nijeriya sun koka game da rashin kula da walwalarsu
2018-07-09 10:13:03 cri
Hukumar kula da wasannin tsalle-tsalle da guje-guje ta Nijeriya AFN, ta soke wata gasa da aka shirya yi a Abuja babban birnin kasar, biyo bayan zanga-zangar da 'yan wasan suka yi, suna masu kokawa da rashin kula da walwalarsu.

Sunday Adeleye, darakta a hukumar AFN, ya shaidawa manema labarai cewa, matakin ya biyo bayan wani taron gaggawa da kwamitin gudanarwar hukumar ya yi game da zanga-zangar.

An bude gasar wasannin guje-guje da tsalle-tsallen da aka shirya zai dauki kwanaki 3 ne a ranar Asabar a filin wasanni na Abuja, inda 'yan wasan da za su wakilci Nijeriya a gasar wasanni guje-guje da tsalle-tsalle ta nahiyar Afrika za su yi gwaji.

Birnin Asaba na jihar Delta ne zai karbi bakuncin gasar a watan Augusta mai zuwa.

Da farko, 'yan wasan sun rufe hanyoyin wasa a filin na Abuja, inda suke bukatar ganawa da kwamitin gudanarwa AFN domin magance rashin kyan yanayin walwalarsu da kuma gazawa wajen biyan kudinsu na alawus-alawus.

Wasu daga cikinsu sun kuma koka da kyan yanayin walwalarsu a lokacin da suke wasanni a duk wata gasa da hukumar ta shirya.

Sun kuma soki wakilinsu a kwamitin gudanarwar hukumar da gazawa wajen kare muradunsu yadda ya kamata. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China