in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaiministan Sin ya bukaci a karfafa hadin gwiwa don samun kyakkyawar makoma
2018-07-08 15:14:45 cri
Firaiministan kasar Sin Li Keqiang ya bukaci a kara zurfafa hadin gwiwa da bude kofa a tsakanin kasar Sin da kasashen tsakiya da gabashin Turai wato (CEEC), domin samun kyakkyawar makoma da kuma ci gaba.

Li ya yi wannan kiran ne a yayin da ya halarci taron hadin gwiwar shugabannin Sin da kasashen tsakiya da gabashin Turai wato China-CEEC karo na 7 a birnin Sofia, na kasar Bulgaria, inda ya yi maraba da bude kofa, da yin cudanya tare karkashin tsarin na 16+1 don samun nasarori masu tarin yawa karkashin hadin gwiwar bangarorin biyu.

Ya ce tsarin hadin gwiwar Sin da Turai ya kasance wani muhimmin tushe wanda zai kara karfafa amincewa da juna da cin moriyar juna daga dukkan bangarorin da abin ya shafa, kana zai taimaka wajen bunkasa ci gaban dangantakar dake tsakanin Sin da Turai. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China