in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya halarci bikin cika shekaru 40 da kulla yarjejeniyar sada zumunta tsakanin Sin da Japan
2018-05-11 10:58:45 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang, da firaministan kasar Japan, Shinzo Abe, sun halarci bikin cika shekaru arba'in da daddale yarjejeniyar shimfida zaman lafiya da sada zumunta tsakanin Sin da Japan Jiya Alhamis, a birnin Tokyo. Li ya kuma halarci bikin maraba da zuwa Japan da aka shirya masa, gami da gabatar da jawabi, inda mutane daga bangarorin siyasa da tattalin arziki da sauransu kusan dubu biyu suka hallara.

Firaminista Li ya jaddada cewa, yayin ziyararsa Japan a wannan karo, shi da shugaban Japan sun yi waiwaye adon tafiya da takaita nasarorin da suka samu a baya, da cimma matsaya tsakaninsu, kan yadda za a raya huldar kasashen biyu cikin dogon lokaci kuma ta hanyar da ta dace. Suna ganin cewa, akwai sabbin damarmaki wajen kyautata dangantakar Sin da Japan. Firaministan ya ce ya kamata bangarorin biyu su nuna himma da kwazo wajen daukar sabbin matakan inganta huldarsu, da kyautata burin jama'arsu gami da kasashen duniya, kan ci gaban dangantakarsu.

A nasa jawabin kuma, Shinzo Abe ya ce, ziyarar firaministan kasar Sin Li Keqiang a Japan, ta sake maido da dangantakar kasashen biyu kan turba madaidaiciya. Inda ya ce ya kamata kasashen biyu su yi kokari kafada da kafada don warware matsalolin dake gabansu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China