in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya bayyana yakininsa game da tattalin arzikin kasar
2018-07-07 21:01:49 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya bayyana a yau Asabar cewa, tattalin arzikin kasar Sin na da karfin da zai iya ci gaba da tsayawa da kafarsa tare da kara bunkasa cikin sauri don samun ci gaba mai inganci.

Li Keqiang ya bayyana haka ne yayin da yake jawabi ga taro kan kasuwanci karo na 8, da aka yi tsakanin kasar Sin da kasashen tsakiya da gabashin Turai a birnin Sofia na Bulgaria.

Ya ce tattalin arzikin kasar Sin ya ci gaba da samun ingantuwa cikin matsakaicin mataki da sama da kaso 7 cikin dari a shekaru 5 da suka gabata, kuma yana bada gudummawar sama da kaso 30 cikin dari ga ci gaban tattalin arzikin duniya a duk shekara.

Har ila yau, ya ce ma'aunin tattalin arziki wato GDP na kasar Sin, ya karu da kaso 6.8 cikin dari a rubu'in farko na bana, wanda ya dara na makamancin lokacin a shekarun da suka shude.

Firaministan ya kuma jadadda matsayar kasar Sin, na tsayawa kan manufar sauya fasalin kasuwarta da kara bude kofa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China