in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin firaministan kasar Sin Hu Chunhua zai kai ziyara kasar Burkina Faso
2018-07-06 19:50:51 cri
A yau Juma'a, a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa, Mr. Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, bisa gayyatar da gwamnatin kasar Burkina Faso ta yi masa, mataimakin firaministan kasar Sin Hu Chunhua zai kai ziyara kasar Burkina Faso.

Wannan ita ce tawagar wakilan gwamnati ta farko da gwamnatin kasar Sin ta tura zuwa kasar Burkina Faso tun bayan da aka farfado da dangantakar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu a ran 26 ga watan Mayun bana. Wannan ya bayyana cewa gwamnatocin kasashen biyu na muhimmanta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Lu Kang ya kara da cewa, bisa gayyatar da gwamnatin kasar Sin ta yi masa, shugaba Christian Kaboré na Burkina Faso zai halarci taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da za a yi a watan Satumban bana a birnin Beijing na kasar Sin. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China