in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in JKS zai ziyarci Afirka ta kudu domin halartar taron BRICS
2018-06-25 19:17:31 cri
Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Mista Yang Jiechi, wanda kuma shi ne daraktan ofishin lura da harkokin wajen na kwamitin kolin JKS, zai ziyarci kasar Afirka ta kudu, domin halartar taro karo na 8 na kasashe mambobin kungiyar BRICS.

Yayin taron da zai gudana tsakanin ranekun 28 zuwa 29 ga watan nan na Yuni a birnin Durban, ana sa ran mahalartansa za su tattauna game da harkokin tsaro.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Geng Shuang ne ya tabbatar da hakan a yau Litinin, yayin taron manema labarai da aka saba shiryawa a nan birnin Beijing.  (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China