in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rouhani: Janyewar Amurka daga yarjejeniyar nukiliyar Iran ba zai amfanawa kowa ba
2018-07-05 11:00:30 cri

Shugaban kasar Iran Hassan Rouhani, ya sanar a jiya Laraba a birnin Vienna, cewar babu wani bangare da zai amfana daga janyewar da kasar Amurka ta yi daga yarjejeniyar makaman nukiliyar kasar Iran.

Ya ce "Ko ita kanta Amurka, ko wata kasa ta daban babu wadda za ta amfana daga janyewar yarjejeniyar makaman nukiliyar kasar Iran".

Ya fadawa taron manema labarai cewa, Iran ta amince da cigaba da bayar da hadin kai game da yarjejeniyar, kuma za ta sauke nauyin dake wuyanta, idan har sauran bangarorin da abin ya shafa sun kiyaye moriyar kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China