in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran za ta sake gudanar da aikin tace sinadarin Uranium idan aka soke yarjejeniyar batun nukiliya na Iran
2018-06-14 13:46:59 cri
Kakakin hukumar makamashin nukiliya ta kasar Iran Behrouz Kamalvandi ya bayyana a jiya Laraba cewa, idan aka soke yarjejeniyar batun nukiliya na kasar Iran, kasar za ta sake gudanar da aikin tace sinadarin Uranium a kamfanin Fordow.

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar a ranar 8 ga watan Mayu cewa, kasar Amurka ta janye daga yarjejeniyar batun nukiliya na kasar Iran, tare da sake sakawa kasar Iran din takunkumin da aka soke shi domin yarjejeniyar batun nukiliyar. Kasar ta Iran ta bayyana cewa, za ta kiyaye bin yarjejeniyar a wannan lokaci tare da yin shawarwari da sauran bangarorin da suka daddale yarjejeniyar, amma idan ba a tabbatar da moriyar kasar Iran da aka kayyade a cikin yarjejeniyar ba, hukumar makamashin nukiliya ta kasar Iran zata sake gudanar da aikin tace sinadarin Uranium. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China