in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: Fadar shugaban kasa ta gayyaci babban sifeton 'yan sanda game da boren jami'an rundunar
2018-07-03 10:15:20 cri
Fadar gwamnatin tarayyar Najeriya ta gayyaci babban sifeton 'yan sandan kasar Ibrahin Idris, domin jin dalilin da ya sanya wani rukuni na 'yan sandan kasar suka yi bore, a birnin Maiduguri fadar mulkin jihar Borno mai fama da kalubalen tsaro.

Rahotanni sun bayyana cewa, 'yan sandan sun yi bore ne bisa zargin rashin biyan su hakkokinsu na albashi, da alwasu-alwasu. Sai dai jim kadan da aukuwar al'amarin, rundunar 'yan sandan kasar ta fidda wata sanarwa dake karyata aukuwar boren.

Sanarwar da kakakin rundunar Jimoh Moshood ya rabawa manema labarai, ta ce 'yan sandan sun gabatar da korafin su ne kawai, kuma nan take suka koma bakin aikinsu.

Kaza lika ta bayyana cewa, rashin rattaba hannu kan kasafin kudin shekarar nan ta 2018 ne ya haddasa jinkirin biyan 'yan sandan hakkokin su, kuma da zarar shugaban kasar Muhammadu Buhari ya amince da kasafin, dukkanin matsalolin da ake fuskanta za su zama tarihi.

Wasu rahotanni sun tabbatar da isar babban sifeton 'yan sandan Najeriyar Ibrahim Idris fadar shugaban kasa a jiya Litinin, inda ya yada zango a ofishin sakataren gwamnatin kasar Abba Kyari, gabanin ganawa da shugaba Muhammadu Buhari. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China