in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Barkewar cutar kwalara ta yi sanadin mutuwar dalibai 3, yayin da wasu 27 ke kwance a asibiti a Nijeriya
2018-06-25 09:38:04 cri
Gwamnatin jihar Gombe dake arewa maso gabashin Nijeriya, ta tabbatar da mutuwar wasu dalibai 3, yayin da wasu 27 ke kwance a asibiti, sanadiyyar barkewar cutar kwalara a kasar mafi yawan al'umma a Afrika.

Kwamishinan Lafiya na jihar Kennedy Ishaya, ya ce tuni Gwamnati ta dauki matakan shawo kan cutar da ta barke a jihar a baya-bayan nan.

Kennedy Ishaya, wanda ya ce marasa lafiyar da dukkansu dalibai ne na wata makarantar Islamiyya a Gomben, ya ce gwamnatin na kula da su kyauta, inda ya kara da cewa, an samar musu da isassun magunguna.

Kwalara kwayar cuta ce wadda kan haifar da matsananciyar gudawa da zai iya kai wa ga mutuwa idan ruwan jikin mutum ya kare.

Barkewar cutar abu ne da aka saba gani a Nijeriya saboda rashin kyan tsarukan samar da ruwa, musamman a yankunan dake da cunkoson jama'a. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China