Danladi Ciroma, wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, ya ce harin wanda ya sabbaba kisan mutane sama da 80, ramuwa ce kan wasu hare hare da aka kaiwa Fulanin makiyaya, tare da sace masu shanu.
Ya ce an samu tashe tashen hankula tsakanin manoma 'yan kabilar Berom da Fulani makiyaya. Kuma tabbas an san wadanda suke tada hankula tsakanin al'ummun yankin, sai dai kawai wasu daga 'yan uwan su na ba su kariya. (Saminu Hassan)