in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi liyafar taya murnar bikin bazara na shekarar 2018 a ofishin jakadancin Sin dake kasar Burundi
2018-02-09 20:30:17 cri

A daren jiya ne, ofishin jakadancin Sin dake birnin Bujumbura na kasar Burundi ya shirya liyafar murnar bikin bazara na shekarar 2018, inda wakilan kamfanonin Sin dake kasar, malamai da daliban kwalejin Confucius, da wakilan Sinawa dake kasar Burundi da yawansu ya kai fiye da 200 suka halarci liyafar.

A jawabinsa, jakadan Sin dake kasar Burundi Li Changlin ya bayyana cewa, shekarar 2018 shekara ce ta cika shekaru 55 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Sin da Burundi, kana a shekarar za a shirya taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka a birnin Beijing, kuma kasar Burundi za ta halarci taron, wannan zai taimaka wajen raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi.

Shi ma a nasa jawabin ministan harkokin wajen kasar Burundi Alain Aime Nyamitwe ya bayyana cewa, a shekarun baya baya nan dangantakar dake tsakanin Burundi da Sin na bunkasa yadda ya kamata. Ya ce gwamnatin kasar Sin ta taimakawa kasar Burundi wajen gina fadar shugaban kasar, da samar da hatsi cikin gaggawa da sauransu, wadanda suka taimakawa kasar Burundi sosai. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China