in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya ya kammala ziyarar yini 2 a Morocco
2018-06-12 09:47:50 cri
Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya bar kasar Morocco a jiya Litinin, bayan ya kammala ziyarar yini 2 a kasar, bisa gayyatar Sarki Mohammed na VI.

Yayin ziyarar ta Shugaba Buhari, kasashen biyu, sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyin hadin gwiwa 3, da suka hada da aikin shimfida babban bututun iskar gas da ya ratsa yankunan kasashen 2, da samar da masana'anta a Nijeriya wadda za ta rika samar da sinadarin ammonia da sauran kayayyaki dangoginsa da kuma kafa wani tsari kan koyar da sana'o'in noma da sa ido.

Shugaban na Nijeriya, ya gana da Sarkin Morocco da Firaminista da shugabannin majalisun dokokin kasar 2.

Ya kuma kai ziyara kwalejin horar da limamai da malaman addini ta Sarki Mohammed na VI, kwalejin dake koyar da matsakaitan akidun addinin musulunci, da 'yan Nijeriya da dama ke karatu a nan. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China