in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta samu sabon shugaba
2018-06-25 08:58:08 cri
Jam'iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta tabbatar da zabar Adams Oshiomole, tsohon Gwamnan jihar Edo dake kudancin kasar a matsayin sabon shugabanta.

Oshiomole mai shekaru 66, ya kama rantsuwar aiki ne jiya Lahadi a Abuja, babban birnin kasar, bayan kammala babban taron jam'iyyar na yini biyu.

Babban taron jam'iyyar da aka fara ranar Asabar da ta gabata ya samu halartar shugaban kasar Muhammadu Buhari da manyan jami'an jam'iyyar na kasa da na jihohi.

Oshiomole wanda makusancin Buhari ne a harkar siyasa, ya tsaya neman shugabancin Jam'iyyar ne ba tare da abokin hammaya ba.

Magabacinsa John Odigie Oyegun, wanda shi ma dan jihar Edon ne ya sha suka daga wasu 'yayan jam'iyyar gabanin babban taron. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China