in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a samarwa 'yan takara tsaro a Zimbabwe bayan harin da aka kaiwa shugaban kasa
2018-06-25 19:57:03 cri
Gwamnatin Zimbabwe ta amince ta samarwa daukacin 'yan takarar da za su fafata a zaben ranar 30 ga watan Yuli tsaro na musamman, muddin suna da fargabar fuskantar wata barazana ga rayukan su. Wannan mataki dai ya biyo bayan harin da aka kai wa shugaban kasar mai ci Emmerson Mnangagwa a ranar Asabar.

A jiya Lahadi ne mataimakin shugaban kasar Constantino Chiwenga, ya shaida wa mahalarta gangamin yakin neman zaben da tsagin shugaban kasar mai ci ke gudanarwa a Chitungwiza dake kudancin birnin Harare, cewar harin da wani abun fashewa da aka kai wa shugaban, yayin da yake sauka daga dandamalin da ya gabatar da jawabi a Bulawayo, aiki ne na ta'addanci. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China